Fassara

Tuesday, August 16, 2022

Manufata ga Jihar Jigawa (IV)

 

6 ga Augusta, 2022



Daga: Mustapha Sule Lamido

Kamar koyaushe, zan fara da gode wa dukkan jama’ar Jihar Jigawa bisa goyon baƴan da suke nuna mana. Wannan aiki da nake yi na ware lokaci domin yin bayanin manufofinmu dalla-dalla, ya nuna cewa muna da cikakken shirin tunkarar aikin dake gabanmu. Ina so na jaddada cewa muna da ƙuduri mai ƙarfi, tanadi cikakke da kuma abokan aikin da ake buƙata don aiwatar da waɗannan manufofi. Kuma mun dogara ga Allah domin jagoranci bisa hakan. Ina kira ga dukkan jama’ar Jigawa da su bamu ƙuri’unsu a watan Maris na 2023, Insha Allahu ba zasu yi nadamar hakan ba.

Wannan babi shine tattaunawata ta biyu kuma ta ƙarshe a kan ilimi. Cimma manufofinmu na ilimi yana buƙatar tallafin dukkan masu ruwa da tsaki na gwamnati da masu zaman kansu. Saboda haka ne muke ta tuntuɓar ƙwararru da ƙungiyoyin ɗalibai, malamai, iyaye, lakcarori da ma’aikata. Waɗannan mutane zasu taimaka wajen inganta manufarmu da kuma aiwatar da ita idan mun samu nasara. Don haka, aiki tare dasu tun daga farko zai taimaka ƙwarai wajen kyautata aikin bayar da ilimi.

Idan kuka bamu dama, cikin yardar Allah zamu sake fasalin tsarin karatun Almajiranci domin gyarashi da kuma ingantashi. Farko zamu fara da ƙididdigar yawan makarantun Allo da tsangayu da kuma yawan almajirai da alaramommi a faɗin jihar. Sannan sai mu kafa kwamitin masana wanda zai ƙunshi alarammomi, ma’aikatan ilimi da kuma ƙwararru. Wannan kwamiti zai fito da wani tsari mai ɗorewa kan tsangayu. Dama akwai tsohon tsari na lokacin shugaban ƙasa Goodluck Jonathan wanda jihoji irinsu Sokoto suka ɗora a kai. A ƙetare kuma, na yi bincike a kan tsarin tsangayu a ƙasar Malaysia wanda ya samar da gyara sosai; akwai kuma wasu tsarukan masu kyau a ƙasashen Afrika ta Yamma. Zan miƙa wa wancan kwamiti bayani game da irin waɗannan tsaruka domin mu cimma burinmu na samar da sabon tsarin almajiranci gyararre, tsaftatacce, nagartacce kuma ɗorarre.

Muna da ƙuduri kan ilimin gaba da sakandiri. A yanzu haka muna da manƴan makarantu guda 14, jami’oin Gwamnatin Tarayya guda biyu, ta jiha guda ɗaya da mai zaman kan ta guda ɗaya. Akwai polytechnic guda uku, kwalejin ilimi guda ɗaya, makarantar fasahar sadarwa guda ɗaya, makarantun ilimin kiwon lafiya guda huɗu da kuma kwalejin ilimin shari’a guda ɗaya. Dukkan waɗanda suke mallakar jiha zasu samu cikakkun kuɗin gudanarwa dai-dai da yanayin tattalin arziƙin da muka samu kanmu a ciki kuma zamu ƙarfafesu domin neman haɗin guiwa a ciki da wajen jihar domin samun tallafin yin bincike da nazarce-nazarce ga Malamai da ɗalibai. Gwamnatin Jihar Jigawa zata ƙulla alaƙa da su don aiwatar da bincike da nazarce-nazarcen da zasu taimaki Jihar.

Insha Allahu zamu bada tallafin karatu ga ɗaliban da suke karantar aikin likita, injiniya, aikin lauya da sauran sassa masu muhimmanci ga ci gaban al’umma. Sauran ɗalibai kuma zasu samu tallafi dai-dai da ƙwazonsu. Ɗaliban da suka fita da digiri mai lambar yabo ta ɗaya suna da babbar damar samun aiki a gwamnati ko tallafin ƙaro karatun digiri na biyu a ciki ko wajen Najeriya. Ɗaliban Digirin Digirgir wato Ph.D ƴan asalin Jihar Jigawa waɗanda bincike ko nazarinsu yake da alaƙar kawo mafita ga matsalolin jihar kai tsaye ko ba kai tsaye ba zasu samu tallafin gwamnati.

Rahotanni daban-daban na ciki da wajen ƙasarnan sun nuna adadin waɗanda suka iya cikakken karatu da rubutu a jiharmu bai wuce 25-30%, a tsakanin manya zalla kuma 38.3%. A cewarsu, hakan na nufin Jigawa ce jiha ta huɗun ƙarshe a wannan ɓangare; sauran su ne Taraba, Katsina da Borno. Komai tantamarmu ga sahihancin irin waɗannan rahotanni, ya zama wajibi mu yi aiki tuƙuru don ganin mun shiga cikin sahun jihohi goman farko nan gaba, ko kuma aƙalla mu samu damar kaiwa  adadin waɗanda suka iya karatu da rubutu 50% a cikin shekaru biyar masu zuwa. Ta ɓangaren samun damar shiga makaranta, Jigawa ita ce ta 32 a cikin jihohi 36 da Abuja yayin da kuma muke na 30 a ɓangaren zuwa makarantar kansa. A jimlace, kimanin 60% na ƴan Jigawa basu da ko wane irin shaidar karatu kamar yadda waɗancan rahotanni suka nuna. Waɗannan alƙaluma ne masu ban tsoro da ya kamata mu tashi tsaye domin canzawa cikin gaggawa.

Akwai ƙoƙari da aka yi a baya domin gyara sha’anin ilimi a Jihar Jigawa. Tsakanin shekarar 2007-2015, an gina cibiyoyin Haɓɓane 56 domin ilimin Fulani mata wanda suke ƙari a kan makarantun makiyaya 172. A tsakanin wannan lokaci, an samar da cibiyoyin ilimin manya guda 1,350. An gina makarantu na musamman guda biyu, Makarantar yara masu kaifin basira ta Bamaina da kuma Makarantar Makafi ta Dutse. Bincikenmu ya nuna cewa an yi watsi da mafi yawancin makarantun Haɓɓane da kuma makarantar Makafi ta Dutse. Amma kuma abin farin ciki shi ne, an ƙara yawan cibiyoyin ilimin manya izuwa 1,917 da kuma na ilimin makiyaya zuwa 418. Sai dai kuma suna fama da rashin isassun ma’aikata wanda Insha Allahu muke da ƙudurin samarwa idan mun samu dama.

Matsin tattalin arziƙi da ake ciki yanzu ba lallai ya bari a aiwatar da tsarin ilimi kyauta ga kowa ba duk da son da muke yi wa hakan. Amma dai muna da ƙudurin bai wa yara mata ilimi kyauta har zuwa sakandiri yayin kuma da marayun cikinsu zasu samu har zuwa gaba da sakandiri a faɗin Jiharmu. Zamu duba yiwuwar sauƙaƙawa ko bayar da ilimi kyauta ga ƴaƴan masu buƙata ta musamman.

Zamu ba walwalar malamai muhimmanci sosai domin inganta aikinsu. Zamu yi nazari kan albashin malamai tare da burin ƙarashi da wani kaso dai-dai da yanayin da tattalin arziƙin jihar zai bada dama. Insha Allahu zamu ƙirƙiri alawus-alawus domin ƙarfafar malamai tare da samar da hanyar martaba malaman da suka yi fice wajen riƙe aikinsu da kyau a faɗin jihar. Zamu bada horo kan horo ga malamai domin su faɗaɗa iliminsu yayin da zamu yi ƙoƙarin samar da cikakkun kayan aiki garesu cikin yardar Allah. Zamu samar da damar tattaunawa lokaci-lokaci tsakanin Malaman makaranta da ɓangaren gwamnati game da nasarori ko matsalolin da suke damunsu. Zamu yi amfani da bayanan da muka samu daga tattaunawar domin samar da gyara a gaba.

Zamu dinga shirya gangamin taron shekara kan ilimi wato Jigawa State Annual Education Summit a turance wanda zai gudana tsawon sati guda domin baje kolin ilimi. Wannan taro zai samu gayyatar baƙi daga ko’ina. Burinmu shine, a cikin shekaru 35 masu zuwa, Jigawa zata zamo cikin jihohi biyar mafi ilimi da ci gaban rayuwa a Najeriya kamar yadda manufarmu mai dogon zango ta tanada.


Gobe ta Allah ce
©Santurakin Dutse

Thursday, July 28, 2022

Manufata ga Jihar Jigawa (III)

 

23 ga Yuli, 2022


Daga: Mustapha Sule Lamido

 

Wannan makon, zan fara da miƙa godiya ga dukkan ƴan Jigawa bisa goyon bayan da suke nuna mana, musamman ma waɗanda suke bibiyar manufofinmu ga Jihar. Haƙiƙa kun nuna mana karamci, kuma zan yi amfani da ƙwarin guiwar da na samu daga wannan goyon baya domin ganin ban baku kunya ba idan kuka bani dama. Cikin satuka huɗu da suka gabata, mun karɓi saƙonnin goyon baya, faɗakarwa da hamayya sama da guda 25,000; har yanzu muna nazarin wasu daga ciki domin ɗaukar matakan da suka dace. Muna roƙon ƙarin shawarwarinku, kuma muna son kowa ya tabbatar ya karɓi katin zaɓensa ko yin rajista ga wanda bai yi ba.

Kamar yadda na ambata a baya, tattaunawarmu ta yau, za ta maida hankali kan ilimi wanda shi ne abin da zamu fi bawa muhimmanci idan an zaɓe mu. A cikin jihohin Najeriya 10 mafi ƙarfi a fannin ilimi, guda 7 sune kuma mafi ƙarfin tattalin arziƙi. Wannan yana nufin ilimi shi ne tabbatacciyar hanyar samun ci gaba. A dunƙule, ƙudurinmu ga ilimi yana da kyau, muhimmanci da kuma faɗi. Mun yi tsare-tsare ingantattu a kan kyautata ilimin addini, boko, ilimin manya da ilimi na musamman a matakai daban-daban.

Kasancewar wannan ne karo na farko da zamu fara gabatar da abubuwan da muke da burin yi a aikace da kuma ƙudurorin da muke fatan aiwatarwa kai tsaye, akwai buƙatar na sake jaddada muhimmancin haɗin kan jama’ar Jigawa. Don haka ba zamu ci gaba da tsohuwar al’adar aiwatar da aiyukan gwamnati bisa tsarin masarautu kawai ba, maimakon hakan zamu yi aiyukan a kan gundarin buƙatu da muradan dukkan ƴan Jigawa ba tare da nuna bambanci ba. Idan an zaɓemu; zamu yi amfani da ci gaban ilimi a matsayin ginshiƙin samun haɗin kai.

Idan an zaɓe mu, muna da burin taɓa ko’ina a ɓangaren ilimi bakin gwargwado, amma zamu yi hakan daki-daki a hankali. Akwai aiyukan da zamu iya gamawa, akwai waɗanda kuma zamu assasa fandisho domin wasu su ci gaba. A taƙaice, zamu yi aiki domin inganta manhajar ilimin Islamiyya da kuma sake fasalin ilimin almajirai. Sauran abubuwan sune gyaran makarantu da ma’aikatun ilimi da ɗaukaka darajarsu; ilimi kyauta ga ƴaƴa mata, inganta ilimin yaƙi da jahilci da ilimin makiyaya; tallafin karatu na musamman ga masu karatu a fannonin neman ƙwarewa da kuma na ɗalibai masu hazaƙar lambar yabo ta ɗaya, sai kuma kyautata walwalar malamai da ma’aikatan ilimi.

Saboda muhimmancinsa, dukkanin naɗe-naɗen muƙamai a ɓangaren ilimi zasu gamu da tantancewa mai tsauri. Mutanen da suka fahimci manufofifnmu kuma suke da fasahar ƙirƙiro da wasu dabarun inganta manufofin a karan kansu ne kaɗai zamu naɗa. Ba zan yi gaggawa ko la’akari da siyasa wajen naɗa kwamishinan ilimi ba; maimakon haka, zan ɓata lokaci don bada dama ga waɗanda suke da sha’awa kuma suka cancanta su nema, mu kuma mu aunasu sosai kafin a basu dama.

Zamu ƙarfafi ɓangarorin sa idanu da ingantuwar aiki na ma’aikatun ilimi a matakin jiha da ƙaramar hukuma domin samun ingantacciyar koyarwa. Lokaci lokaci, zan dinga karɓar bayanai da kaina kuma kai tsaye a kan tasirin sauye-sauyen da zamu dinga kawowa. Zan dinga kai ziyarar ba-zata makarantu akai-akai don ganin ko ana bin tsarin kyautata koyo, koyarwa da sauran al’amuran ilimin baki ɗaya. Za a ware sashe na musamman wanda zai samu wakilci daga ofishin gwamna domin karɓar ƙorafe-ƙorafe daga jama’a a kan harkar ci gaban ilimi. Ba zamu yi wasa da ilimi ba.

Idan komai yana tafiya dai-dai, ilimi shi zai ɗauki kaso mafi tsoka a cikin kasafin kuɗin gwamnatinmu na kowacce shekara kuma zamu shawarci ƙananan hukumomi da su yi hakan. Kasancewar kuɗaɗaen gina harkar ilimi basa taɓa yawa, kuma gwamnati ba zata iya ɗaukar dukkan nauyin ba, zamu kafa Gidauniyar Tallafawa Ilimi ta Jigawa wato Jigawa Education Trust Fund (JETFund) a turance. Wannan gidauniya ko asusu zai dinga neman tallafi daga manyan masu taimako, ƴan kasuwa, ƴan kwangila, ƙungiyoyi da ma ɗaiɗaikun jama’a domin tallafa wa ilimi. Saboda a samu gaskiya da riƙon amana, za a tafiyar da wannan gidauniya bisa haɗin guiwar gwamnati da kwamitin amintattu mai wakilcin dattawan Jihar Jigawa.

Bari mu fara da ilimi a matakin farko, yanzu haka muna da makarantun firamare guda 2,490 a garuruwan dagatai 1,154 a faɗin Jiharmu. Zamu haɗa guiwa da malamai da masu ruwa da tsaki wajen auna yanayin da makarantun suke ciki kafin mu shiga aikin gyara da ɗaga darajar waɗanda suka lalace a cikinsu. Zamu yi hakan mataki-mataki inda zamu fara da mafi lalacewa daga nan kuma zamu kafa fandishon ci gaba da gyaran sauran ba tare da ɓata lokaci ba. Burinmu shi ne a cikin shekaru 4, mafi yawan makarantun Jigawa su kasance a cikin yanayi mai kyau. A kowacce mazaɓar Majalisar Tarayya, zamu gina katafariyar makarantar firamare ta gani ta faɗa wacce za ta zamo cibiyar alfaharin ilimi. A hankali kowacce ƙaramar hukuma zata samu irin wannan firamare Insha Allahu.

Yayin da muke gyara tare da gina wasu makarantun, buƙatar malamai zata ƙaru. Muna sane cewa ƙarancin malamai yana daga cikin manyan matsalolin makarantunmu. Don yin maganin wannan, zamu bawa ma’aikatan gwamnatin da basu da wani cikakken abin yi a ofisoshinsu horo domin mayar dasu makarantu. Zamu tabbatar da cewa ƴan bautar ƙasa ta NYSC da aka tura makarantu sun tsaya a kan aikinsu. Haka kuma zamu ɓullo da tsarin malaman wucin-gadi na sa-kai wanda zai ƙunshi ɗaukar matasan da suka kammala karatu kuma suka cancanta aikin koyarwa. Yayin aiwatar da duka waɗannan, zamu fito da wani tsari mai ɗorewa wanda zai kawar da matsalar ƙarancin malamai a makarantu. Daga ciki akwai ɗaga darajar aikin koyarwa ta yadda waɗanda basa ciki zasu yi sha’awar shiga, waɗanda suke ciki kuma baza su yi garajen fita ba.

Makarantunmu na sakandiri suna buƙatar kulawa. Yanzu haka muna da ƙananan sakandiri guda 571 da manya guda 269. Idan muka yi laakari da cewa sama da ɗaliban Jigawa miliyan guda ne suke buƙatar ilimin sakandiri, to zamu ga cewa sun yi kaɗan. Ƴan Jigawa sama da miliyan 3 duk ƴan ƙasa da shekarun haihuwa 15 ne kuma 50% na wannan adadi sun kai shekarun shiga sakandiri. Insha Allahu zamu zaɓi wasu ƙananan sakandiri domin ɗaga darajarsu zuwa babba yayin da zamu gina wasu a hankali. A kowacce shiyyar Majalisar Dattawa, in Allah Ya yarda zamu gina katafariyar sakandiri sha-kundum wacce za a dinga koyar da ɗaliban kimiyya, kwamashiyal, art da fasaha a tsarin kwana da kuma jeka-ka-dawo.

Ilimin islamiyya ya samu kulawa a Jigawa tun bayan dawowar dimokradiyya a shekarar 1999, amma akwai buƙatar ƙarin aiki. Yanzu haka mafi yawancin Islamiyyu suna aiki ne ba tare da cikakken sa idanun gwamnati ba, ƙalilan daga cikinsu ne ma gwamnati ta san da zamansu. Muna da burin basu kulawa kamar na boko. Ta hanyar taimakon Malaman addini da sauran masu ruwa da tsaki, zamu inganta manhajar koyarwa ta Islamiyyu a matsayin wani fandisho na shigar dasu ƙarƙashin kulawar gwamnati bakiɗaya. Da izinin Allah, zamu samar da ƙuduri wanda zai kyautata tare da inganta koyo da koyarwa a isalamiyyunmu a faɗin Jihar.

A jawabina na gaba, zan haska ƙudurinmu na ilimin ƴaƴa mata, yunƙurin farfaɗowa da inganta ilimin yaƙi da jahilci da na makiyaya, samar da tallafin karatu ga ɗalibai masu hazaƙa da kuma shirin kyautatawa malamai tare da kula da walwalarsu.

 

Gobe ta Allah ce

©Santurakin Dutse

Manufata ga Jihar Jigawa (II)

 

8 ga Juli, 2022

 

Daga: Mustapha Sule Lamido


Yau zan fara da roƙon al’umma da su je su karɓi katunan zaɓensu na din-din-din (PVC) a ofisoshin Hukumar Zaɓe dake ɗaukacin ƙananan hukumomi. Waɗanda kuma basu yi rajistar zaɓe ba, su daure su gaggauta yin hakan. Hukumar zaɓe ta INEC ta tsawaita lokacin yin rajistar zaɓe tun daga ranar 30 ga Yuni, 2022. Ina kira ga dukkan ƴan uwana mutanen Jigawa da mu yi amfani da wannan dama domin yin rajista ga wanda ba shi da ita. A yau kimanin katunan zaɓe na din-din-din guda miliyan 20 ne a jibge waɗanda ba a karɓa ba a faɗin Najeriya. Daga watannin Yuni zuwa Disambar 2021, akwai katunan zaɓe 33,183 da ba a karɓa ba a Jigawa kaɗai. Mu yi rajistar zaɓe, ita ce ƴancinmu wajen sauya makomar Jiharmu da ƙasar mu. 

Kafin mu ci gaba, ina so na yi ƙarin haske a kan abubuwa guda biyu; na farko, shawarwarinku zasu iya tasiri wajen kyautata waɗannan manufofi namu, hakan na nufin a koyaushe zamu iya yi musu gyaran fuska su dace da ƙarin buƙatunku da kuke turowa a kullum. Ƙofa a buɗe take don jin naku ra’ayoyin domin sakasu a inda ya dace. Dama ai a zahirin gaskiya manufofin ba wai nawa bane, na mutanen Jigawa ne gabaɗaya. Na biyu, zan ci gaba da tuntuɓar dukkan sassan jama’ar da nake so na hidimtawa saboda ba nine kaɗai na san maganin matsalolin da muke ciki ba. Wannan na nufin, ba wai burina in yi mulki  a Jigawa ba, burina shine mu haɗu daku tare don kai wa ga ci.

Don cimma burukanmu na ci gaban Jigawa, za mu buƙaci haɗin guiwa da masu ruwa da tsaki a ciki da wajen ƙasarnan. Saboda haka, tuni na fara tattaunawa da Shugaban ƙasar gobe Insha Allah, Maigirma Atiku Abubakar kan buƙatar ba wa Jigawa kulawa ta musamman idan Allah Ya sahale masa. Sannan na fara ɗaukar matakai domin samun cikakkiyar fahimta kan yadda za a samu haɗin guiwa da hukumomi da ƙungiyoyi na ƙasashen duniya domin ci gaban Jigawa da mutanenta.

Daga bibiyar raayoyin jama’a, na fahimta cewar akwai masu shakku game da yiwuwar ko zamu iya aiwatar da waɗannan manufofi. Wasu masharranta ma har sun rawaito wai mun yi ikirarin gudanar da Jigawa ba tare da kuɗaɗen Gwamnatin Tarayya ba. Wannan ba gaskiya bane; mu ba masu siddabaru bane; abin da muke cewa shi ne muna da tsare-tsaren gajere da dogon zango waɗanda zasu kai Jigawa dukkan wani matakin ci gaba sannu a hankali. Nasarar aiwatar da waɗannan tsare-tsaren kuma zai dogara ne da irin haɗin kai da gogon bayan da jama’a suka bamu.

Yanzu haka an ayyana Jigawa a matsayin jiha ta uku mafi talauci a Najeriya inda 87.2% na mutanen ta suke cikin matsin rayuwa. Wannan wani abin takaici ne da ya kamata mu yi aiki tuƙuru tare domin canzawa. ƙiyasin ƙiddigar jama’a na 2022 ya nuna Jigawa tana da mutane 6,842,307, kenan jiharmu tana da isassun jama’ar da zasu iya canza makomarta. Idan da zamu ci nasarar ɓullo da wani yanayi da zai tallafawa mutane miliyan ɗaya kacal su dinga samun ƙarin N3,000 duk sati daga cikin kasuwancinsu, jimilla zasu samar da naira biliyan 3 a sati ko kuma naira biliyan 12 a wata. Wannan adadi ya ninka naira biliyan 5.6 da Jigawa ta karɓa daga Gwamnatin Tarayya a watan Yulin 2021 sau biyu da kusan kwata. Zamu iya cimma wannan tare.

Yanzu haka, muna da ayari na ƙwararru waɗanda suke tattara mana bayanai kan buƙatu da matsalolin ƙananan hukumomi 27. Zamu tsananta tara waɗannan bayanai idan mun ci zaɓe. Da zarar an rantsar damu wanda hakan zai bamu damar sanin muhimman bayanan sirri na gwamnati, zamu auna halin da Jigawa take ciki. Da zarar mun yi wannan, zamu saki jadawalin aiwatar da manufofin a cikin ƴan satuka. Waɗannan zasu yi tasiri kan lokacin da zamu ɗauka wajen aiwatar da manufofinmu. Kamar yadda na faɗa a baya, abin ba siddabaru ko aikin kwana guda bane.

Mataki na gaba shi ne gaggauta zaƙulo mutane masu kishi, jajircewa da ƙwarewa waɗanda zamu yi aiki dasu. Alhamdulillah, mataimakina Dr. Babandi Ibrahim Gumel ƙwararre ne, wanda tare da shi tunma daga yanzu mun fara rubuta sunayen nagartattun mutanen da zamu iya aiki da su. Damuwarmu ita ce ƙwarewarsu da kishinsu ba wai shahara ko buwayarsu ba. Zamu ɓullo da hanyar tantance ƙoƙarin jami’an gwamnati lokaci-lokaci, kuma za a maye gurbin duk wanda ba ya aiki yadda ya kamata. Babu wanda zai zama shafaffe da mai matuƙar ba Jigawa ce a gabansa ba.

Tunanin cewa haɗin kai ba zai samu ba Jigawa, wannan munana zato ne. Da zarar mun kafa amintacciyar gwamnati mai adalci ga kowa, za a samu dunƙulewar mutane domin kawo ci gaba. Haɗa kan mutane ba wai yana nufin kawar da bambance-bambancen dake tsakaninsu bane, yana nufin basu ƙwarin guiwa da tausasarsu ta yadda waɗancan bambance-bambance ba zasu hanasu yin aiki tare wajen ci gaban al’ummarsu ba. Muna da manufofi kaifiyyan kan haka waɗanda a yanzu ba zamu fito dasu fili ba sai lokacin ya yi. Zamu inganta mulki a ƙananan matakai ta hanyar tabbatar da gwamnatocin ƙananan hukumomi masu ƴanci da tsari. Zamu sake fasalin ma’aikatun gwamnati domin rage ɓarna, inganta aiki da mayar dasu hadiman al’umma ba na wasu tsirarun mutane ba.

Ina sane da fargabar wasunmu game da ƙwarewata. Ina da abubuwa guda uku da zan faɗa kan wannan. Farko dai, aikin gwamnati ko riƙe tarin muƙamai ba shi ne kaɗai ma’aunin ƙwarewa  Misali, da yawa basu taɓa shiga gwamnati ba, amma suna da baiwa iri-iri. Shugabanci ba aikin ofis bane kawai, ƙwararren ma’aikacin gwamnati zai iya zama rarraunan shugaba. Abu na biyu, a Najeriya tun 1999 mun ga yadda aka zaɓi ma’aikata da waɗanda suka re tarin muƙaman gwamnati tsawon shekaru amma basu tsinana abin kirki ba. Marigayi Abubakar Rimi ya zama gwamnan tsohuwar Jihar Kano yana ɗan ƙasa da shekaru 40 a lokacin da wasu suke ganin bai ƙware ba, amma ya zamo babban abin alfahari a tarihin Najeriya. Na uku, sarrafa kujerar gwamna ba aikin mutum guda bane. Kujera ce da ake gudanar da ita da taimakon Majalisar Zartarwa da ma’aikatan gwamnati tare da sa idanun Majalisar Dokoki da ɓangaren Shari’a. Gwamna ba wai mutum ne da yake da ikon yin abin da ya ga dama ko yanke hukunci shi kaɗai kai tsaye ba.

Da wannan, ina ganin na kammala muƙaddimar manufofina ga Jihar Jigawa. Nan gaba, zan maida hankali kai tsaye wajen bayanin gundarin abubuwan dake gabanmu waɗanda muke sa rai zasu kai jiharmu ga ci. Kan gaba a wannan batutuwa shi ne ilimi, sannan ilimi sannan kuma ƙarin ilimi. Na gode.

    

Gobe ta Allah ce

©Santurakin Dutse